Rikicin kasar Somalia
November 11, 2007Talla
Dubun dubatan mutane na tserewa daga Mogadishu babban birnin kasar Somalia yayin da ake ci-gaba da gwabza kazami fada mafi muni a cikin wannan shekara. Yanzu haka dai yawan wadanda aka kashe a artabun da aka shafe kwanaki ana yi tsakanin dakarun Ethiopia dake goyawa gwamnatin Somalia baya da sojojin sa kai na ´yan Islama ya kai mutane 80. A jiya asabar an dan samu kwarkwaryar kwanciyar hankali a babban birnin wanda yaki ya yiwa kaca-kaca. Likitoci sun ce suna fama da matsaloli wajen kula da mutanen da suka jikata saboda karanci magunguna da rashin gadaje a asibitoci.