1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin makaman nuklear Iran

June 1, 2007
https://p.dw.com/p/BuK9

Kasar Iran, ta bayyana aniyar komawa tebrin shawarwari tare da hukumar yaƙi da yaɗuwar makaman nuklea ta MDD.

Ta bayyana hakan, a sakamakon ganawar da aka yi jiya, tsakanin sakataran harakokin wajen ƙungiyar gamayya turai Havier Solana, da kuma shugaban tawagar Iran a tanttanawar rikicin nuklea Ali Larijani.

Solananya bayyana gamsuwa, a game da ci gaban da aka samu a wannan badaƙala.

Idan dai ba a manta ba, ƙasar Iran ta yi tsayuwar gwamen jaki, a game da buƙatocin Majalisar Ɗinkin Dunia na ta yi watsi da aniyar mallakar makaman nuklea.

Tawagogin 2, sun yanke shawara sake gamuwa, nan da makwani 2 masu zuwa, domin ci gabada tantanawa.

Saidai a yayin da ta ke maida martani, sakatariyar harakokin wajen Amurika, Condoleesa Rice, ta ce, ci gaban da a ka ce an samu a taron na jiya, irin na mai haƙar rijiya ne.