1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin siyasa a Turquiyya

May 6, 2007
https://p.dw.com/p/BuLy

Ministan harakokin wajen ƙasar Tukiyya, bugu da ƙari ɗan takara a zaɓen shugaban ƙasa, ya ga samu ya ga rashi.

Jam´iyar AKP ce,mai riƙe da ragamar mulki, ta ajje takara Abdallah Gul, gaban majalisar dokoki, amma duk da rinjaye ta, zaɓen ya gagara.

A zagayen farko, na ranar 27 ga watan Aprul, Kotin ƙoli ta rushe zaɓen, dalili da rashin samun issasun yan majalisa a lokacin kaɗa ƙuri´a.

Bisa dokokin tsarin mulkin ƙasar Turkiyya, cilas !!! sai a ƙalla kashi 2 bisa 3, na yan majalisa sun yi zaɓe, kamin ya sa mu karɓuwa.

Yau ne lahadi a ka buƙaci shirya zagaye na 2, amma shugaban majalisar ya tada taron, dalili da rashin samun addadin yan majalisar da ya cencenta.

Cemma kamin zaɓen jam´iyun adawa, sun ambata ƙaurace masa.

A hira da yayi da manema labarai, Abdallah Gul,ya ce zai janye takara sa, muddun bai ci nasara ba a zaɓen na yau.

Wannan zaɓe ya saka Turkiya a cikin wani hali na rikicin siyasa, wanda a sakamakon sa,gwamnati ta yanke shawara shirya zaɓen majalisar dokoki,na kamin lokaci, ranar 22 ga watan juli, tare da ɓullo da wasu dokokin kwaskarima, ga kundin tsarin mulki na ƙasa.