1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rundunar MDD ta gama aiki a kasar Haiti

Salissou Boukari
October 6, 2017

Bayan shekaru 13 ta na ayyukan samar da tsaro, rundunar Majalisar Dinkin Duniya a kasar Haiti ta Minustah ta kawo karshen aikin duk da cewa akwai rikici na siyasa a kasar.

https://p.dw.com/p/2lMGq
Haiti UN Mission Blauhelme UN Mission
Dakarun Majalisar Dinkin Duniya a kasar Haiti sun gama aikiHoto: picture-alliance/AP Photo/D.N.Chery

Shugabar rundunar ta Majalisar Dinkin Duniya a kasar ta Haiti Sandra Honore ta ce har yanzu akwai sauran ayyuka da dama da ta kamata a yi a kasar ta Haiti kafin ta kai matsayin da kowane dan kasar ke fatan gani.

A shekara ta 2004 ne dai aka girka rundunar ta Majalisar Dinkin Duniya a kasar ta Haiti bayan ficewar shugaban kasar Jean-Bertrand Aristide domin kwantar da tashe-tashen hankulan da aka fuskanta musamman a Port-au-Prince babban birnin kasar, sai dai kuma rundunar ba ta samu yarda daga 'yan kasar ba, musamman magoya bayan tsohon shugaban kasar.