1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ruwan sama sun kashe mutane 78 a China

Gazali Abdou TasawaJune 23, 2016

Rahotanni daga China na cewa mutane 78 sun hallaka a yayin da wasu 500 suka jikkata a sakamakon wasu ruwan sama kamar da bakin kwarya da kankara da aka yi a birnin Jiangsu na Gabashin kasar.

https://p.dw.com/p/1JCAy
China Hochwasser
Hoto: AP

Kamfanin dillancin labaran kasar ta China ya ruwaito cewar ruwan saman ya kuma tafi da gidaje da dama a birnin Yancheng. Yankunan kasar ta China da dama ne dai suka fuskanci ruwan sama mai tsananin gaske a wannan mako.

Abin da ya haddasa asarar rayuka da dama, da ta kadarori da aka kiyasta darajarsu a miliyan 410 na Dalar Amirka, a yayin da mutane dubu 200 suka rasa muhallansu.