1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rwanda ta janye jakadanta daga Faransa

November 24, 2006
https://p.dw.com/p/BuaX

Kasar Rwanda ta janye jakadanta daga Faransa sannan ta yi barazanar katse huldodin diplomasiya da Faransa. Hakan dai ya zo ne bayan da wani alkali a Faransa ya ba da takardar kame jami´an Rwanda su 9 bisa zarginsu da hannu a kisan kare dangi da aka yi a Rwandar a shekara ta 1994. dukkan mutanen su 9 na kurkusa ne da shugaba Paul Kagame, wanda alkalin ya ce ya zarga da hannu dumu-dumu wajen harbo jirgin saman da tsohon shugaban kasar Juvenal Habyarimana ke ciki. Mutuwar shugaban ne kuwa ta janyo kisan kare dangin da aka yiwa dubun dubatan ´yan Tutsi da kuma ´yan Hutu masu sassaucin ra´ayi. Shugaba Kagame ya yi watsi da zargin da alkali Jean-Luis Bruguiere yayi da cewa da akwai wata manufa ta siyasa a ciki. Dangantaka tsaakanin Faransa da Rwanda ta yi tsami, inda shugaba Kagame ke zargin Faransar da rashin yin wani abin kirki na hana aukuwar kisan kiyashin.