Sa hannu kan kudurin zaman lafiya a Kwalombiya
November 23, 2016Talla
Yarjejeniyar farko dai an yi watsi da ita lokacin zaben raba gardama a watan Oktoba, inda masu zabe suka nuna cewa an yi fifiko ga 'yan tawaye cikin kudurin. Sai dai kudurin da aka yi wa dan kwaskwarima, wanda za a sanya wa hannu a ranar Alhamis a Bogotá, babban birnin kasar, kusan kananan gyare-gyare ne kawai aka yi masa. An kuma bayyana cewa a wannan karon ba a bukatar 'yan kasa su yi kuri'a, illa kawai za a mika wa majalisar dokoki ta yanke hukunci a kai. Akalla mutane dubu 220 suka mutu a yakin basasan kasar ta Kwalombiya.