1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabbin hare-hare a Najeriya

April 24, 2017

Masu aikin ceto da jami'an tsaro sun tabbatar da asarar rayuka a wasu jerin hare-haren da wasu 'yan mata uku da namiji daya suka kai wasu yankuna da ke bayan garin Maiduguri.

https://p.dw.com/p/2boZQ
Nigeria Selbstmordanschlag in Zabarmari
Hoto: picture alliance/AA/M. Abba

Rahotannin da ke fitowa daga arewa maso gabashin Najeriya, na cewa wasu mutane bakwai sun mutu a wasu hare-haren kunar bakin wake da ake alakantasu da mayakan Boko Haram. Masu aikin ceto da ma jami'an tsaro sun ce harin farko ya auku ne a kauyen Mammanti mai tazarar kilomita 15 a gashin birnin Maiduguri.

A cewarsu wasu 'yan banga sun yi kokarin dakatar da wasu 'yan mata uku dake dauke da bama-bamai da asubahin yau, inda biyu daga cikinsu suka tarwatsa kansu, dayar kuwa soja ya harbe ta. An kuma sami wani dan banga daya da ya rasa ransa a harin.

Akwai ma wani dan kunar bakin waken namiji da ya shiga kauyen Mainari da ke yammacin birnin Maiduguri, ya kuma kashe 'yan banga uku tare da raunata wasu biyu.