1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabon rahoton hukumar IAEA kan shirin nukiliyar Iran

November 16, 2007
https://p.dw.com/p/CHv1
Ƙakashe da dama sun mayar da martani daban daban a kan sabon rahoton da hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa IAEA ta bayar game da shirin nukiliyar nukiliyar Iran da ake takaddama a kai. Ƙasashen Amirka da Birtaniya sun sanar da cewa zasu ƙara matsa kaimi wajen faɗaɗa takunkumai akan hukumomin birnin Teheran. Su kuwa a nasu ɓangaren hukumomin na Iran sun ce rahoton na birnin Viennen ya karfafa manufofin su. A cikin rahoton hukumar ta IAEA ta ce Iran ta miƙa gamasassun bayyanai dangane da shirin ta na nukiliya. To sai dai har yanzu tana ci-gaba da yin kunnen uwar shegu ga bukatun MDD na ta daina sarrafa sinadarin uranium.