1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

A kalla mutane 36 ne aka hallaka yayin da 80 suka jikka ta

Kamaluddeen SaniSeptember 27, 2015

Jami'an lafiyar birnin Bangui na kasar suka ce tuni aka fara kulawa mutane 80 din da suka sami raunuka a asibiti a yayin da 36 suka rigamu gidan gaskiya.

https://p.dw.com/p/1GeOh
Zentralafrikanische Republik
Hoto: Getty Images/AFP/Pacome Pabandji

Mai magana da yawun wata tawagar musulmai a yankin da rikicin ya faru Osmane Abakar yace, yamutsin ya kaure ne bayan gano wata gawa ta musulmi da ya mutu a wani masallaci dake a bangaren Kristocin, wanda hakan ya harzuka musulmin kai wani hari akan kristocin yankin a ranar a sabar.

Suma daga bisani Kristocin suka mayar da martani a ranar lahadin nan da yayi sanadiyar mutuwar mutane da dama.

Jami'an lafiyar birnin Bangui na kasar suka ce tuni aka fara kulawa mutane 80 din da suka sami raunuka a asibiti a yayin da 36 suka rigamu gidan gaskiya.

Tuni dai mahukuntan Jamhuriyar Afrika ta Tsakiyar dake fuskantar tashe -tashen hankulan addini ta ayyana dokar tabaci a yankin da al'amarin ya faru.