1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabon shugaban kasa a Somaliya

Yusuf Bala Nayaya
February 8, 2017

Tsohon Firaministan Somaliya Mohamed Abdullahi Farmajo ya zama sabon shugaban kasar, a yayin zaben da majalisar dokokin kasar ta gudanar.

https://p.dw.com/p/2XBsB
Sabon zababben shugaban kasar Somaliya Mohamed Abdullahi Farmajo
Sabon zababben shugaban kasar Somaliya Mohamed Abdullahi FarmajoHoto: REUTERS/F. Omar

An zabi tsohon Firaministan Somaliya Mohamed Abdullahi Farmajo a matsayin sabon shugaban kasa, a yayin zaben da majalisar dokokin kasar ta gudanar. Rahotanni sun nunar da cewa tuni shugaban kasar mai ci Hassan Sheikh Mohamud wanda a zage na farko ya samu rinjaye kafin zaben ya sauya akala a zagaye na biyu, ya amince da shan kaye. Farmajo ya samu nasarar ne bayan da aka gudanar da zagaye na biyu a zaben, bayan da aka rasa wanda ya samu nasara a tsakaninsa da shugaba mai ci Hassan Sheikh Mohamud a zagaye na farko. Kamfanin dillancin labaran Reuters dai ya ce anjiyo harbe-harben bindiga a daf da fara zagaye na biyu na zaben.