1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kasashen EU na neman mafita kan batun 'yan gudun hijira

Lateefa Mustapha Ja'afarJune 22, 2016

Kasashen kungiyar Tarayyar Turai wato EU sun amince da sabon tsarin tsaron kan iyakokin kasashen na bai daya.

https://p.dw.com/p/1JBXJ
Shirin tsaron kann iyaka na kungiyar EU
Shirin tsaron kann iyaka na kungiyar EUHoto: Getty Images/AFP/D. Dilkoff

Sabon shirin wanda zai dora a kan shirin tsaron gabar tekun kan iyakokin kasashen na Frontex, zai fara aiki ne daga lokacin bazara na wannan shekara, da nufin kare kan iyakokin kasashen na EU. A karkashin shirin dai za a dauki ma'aikata kimanin 1000 da kuma masu tsaron kan iyakokin kasashen 1 500. Wannan sabuwar yarjejeniya dai za a fara aiki da ita da zarar majalisar ministocin Tarayyar Turan ta amince da shi.