1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sakamakon zaɓen raba gardama a ƙasar Kenya

Umar Saleh SalehAugust 5, 2010

Jama'a sun amince da a kawo sauye sauye na tsarin siyasa a ƙasar Kenya

https://p.dw.com/p/Ocfc
Hoto: AP

Sakamakon wucin gadi na ƙuri'ar raba - gardamar da al'ummar Kenya ta ka'ɗa a  jiya Laraba cikin ƙwanciyar hankali,

ya nunar da cewar, ra'ayin 'yan ƙasar ya karkata ne ga sake fasalin tsarin siyasar ƙasar, wadda ke kan gaba wajen ƙarfin tattalin arziƙi a  yankin  ƙasashen gabashin Afirka.

A cikin sakamakon da hukumomin ƙasar suka wallafa a wannan Alhamis  ya nuna cewa kusan kashi 70 cikin ɗari na al Ummar ƙasar

 sun  goyi bayan samar da sauye sauye ga yadda ake tafiyar da harkokin siyasar ƙasar.

 Sauye sauyen dai sun haɗar da rage ƙarfin ikon shugaban ƙasa da ƙara bada fifiko ga shugabanci a yankunan karkara,

kana da warware batun cin hanci da rashawa da kuma matsalar ƙabilanci a ƙasar- matsalolin da kuma ke janyowa ƙasar ta Kenya cikas tun sa'adda ta sami 'yanci daga ƙasar Birtaniya a shekara ta 1963. 

Mawallafi : Abdopurahamane Hassane

Edita        : Mohammed Awal  Nasiru