Ci gaba da laluben jirgin Malesiya da ya bace
August 10, 2015Talla
Tiong Lai ya ce wata tawagar kasar ta Malesiya za ta fara gudanar da bincike domin tan-tance ko tarkacen jirgin na da alaka da jirgin Malesiyan da ya bace tsahon sama da shekara guda, kafin daga bisani a kara fadada bincike.
Lai wanda bai yi karin haske ba game da irin tarkacen jirgin da aka gano, ya bukaci dukkanin wadanda suke da alaka da binciken da su bi sannu a hankali.
Tuni dai mahukuntan kasar Malesiyan suka bukaci tallafin wasu kasashen yayin da Faransa ta aike da wani jirgi da kuma kwale-kawale domin gudanar da bincike.