1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Saliyo; An fara zaman makoki na mako daya

August 16, 2017

Gwamnatin kasar Saliyo ta sanar da zaman makoki na mako daya domin jimamin mutanen da suka rasu a ambaliyar ruwa.

https://p.dw.com/p/2iLX4
Sierra Leone Überschwemmungen Erdrutsch Leichenhalle
Hoto: picture-alliance/AP/Society 4 Climate Change Communication

Al'ummar kasar Saliyo sun fara zaman makoki na kwanaki bakwai a yau laraba domin jimami da nuna alhini ga mutanen da suka rasa rayukansu a ambaliyar ruwa da zaftarewar kasa da suka yi sanadiyar mutuwar daruruwan jama'a.

Da yammacin yau za'a gudanar da taron addu'oi na mabiya addinai daban daban a babban filin wasa dake Freetown babban birnin kasar inda iftila'in ya auku.

Ya zuwa yanzu an an gano gawarwakin mutane 297 da suka hada da kananan yara 109.

Ba dai kai ga tantance adadin mutanen da suka rasu ba. Da farko dai ministan lafiya na kasar yace adadin ya kai mutum 500 yayin da dama kuma har yanzu ba'a gano su ba.

A gobe Alhamis za'a yi jana'izar mamatan.