1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Moroko ta jaddada aniyarta ta shiga kungiyar Tarayyar Afirka

Salissou Boukari
November 7, 2016

Shugaban kasar Maroko sarki Mohammed na shida da ke ziyara a kasar Senegal ya yi jawabinsa na shekara-sheraka da yake yi na gadon mulkinsa daga birnin Dakar na kasar ta Senegal.

https://p.dw.com/p/2SFx7
Saudi-Arabien Riad GCC Mohammed Ben Al-Hassan
Hoto: picture alliance/AA

Cikin jawabin da 'yan kasar ta Maroko suka kalla da kuma sauraro kai tsaye ta kafofin yada labaran kasar, Sarki Mohammed na shida ya ce ya yi hakan ne domin nuna yadda kasar ta Maroko take da babbar bukatar sake shiga cikin 'yan uwanta na Afirka inda yake cewa:

" Ganin yadda na ke yi muku wannan jawabi mai tarihi na shekara-shekara daga nan Dakar babban birnin kasar Senegal, na san wannan mataki nawa ba zai baku mamaki ba, domin kasar Senegal na daga cikin kasashen da suka taka rawar gani cikin tarihin wannan kasa tamu tare da sauran kasashen Afirka da ma na Larabawa."

Sarkin na Maroko ya kara jaddada aniyar kasar ta shi ta sake dawowa cikin 'yan uwanta kasashen Afirka. Wannan ziyara ta kasar Senegal na zuwa ne bayan da ya ziyarci kasashen Ruwanda da Tanzaniya da ke yankin Gabashin Afirka, inda yake fatan ganin kasar ta samu komawa cikin kungiyar Tarayyar Afirka ba da jimawa ba.