A cikin shirin za a ji hukumomin Jihar Diffa a Jamhuriyar Niger dake fama da rikicin Boko Haram sun gargadi mayakan kungiyar da ke cikin daji da su dawo su mika makaman su kafin ranar 31 ga watan Oktoba. Gwamnatin jihar Filato a Najeriya ta kudiri aniyar gano 'yan bindigar da ke kai hare hare a karamar hukumar Bassa.