1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shirin rufe tashar nukiliyar Koriya ta arewa

July 14, 2007
https://p.dw.com/p/BuGN

Jamian binciken na hukumar makamashin nukiliya ta majalisar ɗinkin duniya sun sauka Koriya ta arewa a matakin fara aiwatar da shirin rufe babbar tashar nukiliyar ta dake yongbyon. Wannan dai shine karon farko da jamián binciken suka kai ziyara cibiyar tun cikin shekara ta 2002. A waje ɗaya kuma sahun farko na mai da aka yiwa Koriya ta arewan alƙawari ya isa ƙasar. A yau da sanyin safiya jirgin ruwan koriya ta kudu dake dauke da man ya sauka tashar jiragen ruwa na koriya ta arewa. A ƙarƙashin yarjejeniyar da aka cimma, Koriya ta arewa tace zata rufe tashar nukiliyar ta Yonbiyon da zarar ta sami man da aka alakawurta mata daga makwabciyar ta koriya ta kudu.