1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shirin yafewa kasashe matalauta bashi ya fara aiki

January 6, 2006
https://p.dw.com/p/BvDW

A yau hukumar bayarda lamuni ta duniya ta sanar cewa daga jiya alhamis shirin yafewa kasashe mafiya talauci a duniya 19 basusuka dake kansu ya fara aiki.

Kakakin hukumar yace yafe bashin, karkashin wani shiri na kasashe 8 masu arzikin masanaantu ya fara aiki wanda hakan ya nuna bashin ya tafi nan take daga kann kasashen da aka amince zaa basu wannan sauki.

A ranar 21 ga watan disamba daya gabata ne hukumar gudanarwa ta IMF ta amince yafe bashin dala biliyan 3 da digo 3 da ake bin kasashe matalauta da suka hada wasu kasashen nahiyar Afrika guda 12,ciki kuwa har da Ghana Nijar Burkina Faso da Senegal da Mali.