1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shirin zaman lafiya a Yankin Gabas Ta Tsakiya

Ibrahim SaniJanuary 1, 2008
https://p.dw.com/p/CifZ

Anyi taho mu gama a tsakanin ´yan jam´iyyar Fatah ta Mahmud Abbas da kuma ´yan ƙungiyyar Hamas a Gaza. Hakan ya haifar da asarar rayuka shidda, a hannu ɗaya kuma da jikkatar wasu 30. Al´amarin yazo ne bayan Mr Abbas ya ƙara nanata aniyarsa na gudanar da zaɓe ne a yankin. A jawabinsa na bikin cikar Jam´iyyar ta Fatah shekaru 43, Mr Abbas ya ce hakan zai kawo ƙarshen rikice-rikice da tashe-tashen hankula a yankin. Bugu da ƙari shugaban ya kuma buƙaci yin sulhu a tsakanin ɓangarorin biyu. Samun hakan a cewar Abbas, abune da zai taimaka, wajen samun sauƙin warware rikicin dake tsakanin yankin da Israela.