1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaba Jacob Zuma ya tsallake rijiya da baya

Kamaluddeen SaniApril 6, 2016

A cigaba da tirka-tirkar data dabai baye shugaba Jacob Zuma sakamakon badakalar gyaran gidan sa, yanzu haka 'Yan majalisar Dokokin kasar Afirka ta Kudu sun kada kuri'ar kin amincewa da tsige shi daga mukamin sa.

https://p.dw.com/p/1IQ6o
Afrika Jacob Zuma
Hoto: picture-alliance/dpa/S. Hisham

Shugaban ya tsallake rijiya da baya ne sakamakon wani zama da 'yan majalisar Dokokin kasar suka yi bayan da wata kotun kasar ta kama shi da laifin take tanede-tanden kundin tsarin mulkin kasar ta yin amfani da kudaden gwamnati don gyara wani katafaren gidansa.

Tun dai a kwanakin baya ne wata hukuma a kasar ta Afrika ta Kudun ta futar da wani rahoto da ke nuni da cewar Shugaba Zuman yayi amfani da makudadan kudaden gwamnati wajen gyara gidansa da ke a yankin Kwazulu Natal, a inda gyare-gyaren suka hada da samar da katafaren wajen wanka da dakin saukar baki wanda shugaba Jacob Zuma yayi mursisi wajen kin mutunta sakamakon rahoton.