1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar: Tayin gwamnatin hadin kan kasa

Yusuf BalaMarch 23, 2016

Mahamadou Issoufou ya ce a kwai bukatar hadin kan 'yan adawa wajen ciyar da kasar gaba a fannoni na tattalin arziki da zaman takewa.

https://p.dw.com/p/1IITz
Niger Präsident Mahamadou Issoufou
Shugaba Mahamadou IssoufouHoto: Seyllou/AFP/Getty Images

Shugaba Mahamadou Issoufou da aka sake zabe a jamhuriyar Nijar a zangon wa'adi na biyu bayan zaben da ke cike da cece-ku-ce a ranar Laraban nan ya yi tayi na gwamnatin hadin kan kasa tare da 'yan adawa, wadanda suka kaurace wa zaben da aka yi zagaye na biyu a karshen makon da ya gabata.

A wata zantawa da shugaban ya yi da kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP ya bayyana cewar a shirye yake ya yi gwamnati ta hadin kan kasa tare da 'yan adawar dan a tinkari matsaloli da al'ummar kasar ta Nijar ke fiskanta.