1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban Tunisiya zai gana da ma'aikata

Abdul-raheem Hassan
January 13, 2018

Shugaban kasar Tunisiya Beji Caid Essebsi ya bukaci tattaunawa da jam'iyun adawa da kungiyoyin fararen hula a wani mataki na kwantar da zanga-zangar adawa da tsarin gwamnati.

https://p.dw.com/p/2qnU2
Tunisia 2020
Hoto: picture-alliance/dpa/M. Messara

Wasu manyan birane Tunisiya sun barke da zanga-zanga mai tsanani na kusan kwanaki bakwai, da nufin nuna adawa da kara haraji da ya haifar da tsadar rayuwa sakamakon hauhawar farashin kayan abinci da sauran kayan masarufi.

Akalla mutum guda ya rasa ransa a zanga-zangar, amma 'yan sanda sun nesanta kansu da hannu a kisan. Sai dai a yanzu suna tsare da sama da mutane 800 ciki har da jagoran wata jam'iyar adawa bisa zargin tada zaune tsaye.

Tunisiya na shan fama da jerin zanga-zanga a kan karancin rashin ayyukan yi da talauci, abin da ake ganin zai dauki hankalin ganawar shugabannin kwadagon da shugaban kasar Beji Caid Essebsi.