1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugabanni a Kataloniya za su kai kara MDD

Yusuf Bala Nayaya
February 1, 2018

A cewar lauyansu Ben Emmerson tsarewar da mahukuntan kasar Spain suka yi masu an tsarata ne don hana masu dama ta shiga harkokin siyasa.

https://p.dw.com/p/2ruCt
Spanien Sitzung des katalanischen Parlaments in Barcelona
Zaman majalisa a yankin KataloniyaHoto: Reuters/A. Gea

Shugabanni uku daga yankin Kataloniya da aka dauresu a Spain sakamakon shigarsu dambaruwar siyasar yankin a kokarin ballewa daga kasar Spain sun bayyana cewa za su kai kukansu ga 'yan fafutika na Majalisar Dinkin Duniya kamar yadda lauyansu a birnin London ya bayyana a wannan rana ta Alhamis.

A cewar lauyansu Ben Emmerson tsarewar da mahukuntan kasar Spain suka yi masu an tsarata ne don hana masu dama ta shiga harkokin siyasa a matsayinsu na wakilan al'ummar yankin Kataloniya. Lauya Emmerson ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai da ya kira a wannan rana.