1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugabannin EU zasu ɗauki guda kan batun Kosovo

December 14, 2007
https://p.dw.com/p/Cbtc
A taron ƙolin da suka yi a birnin Brussels shugabannin ƙungiyar tarayyar Turai EU sun ƙuduri aniyar cimma matsaya ta bai ɗaya a dangane da batun ´yancin kan lardin Kosovo. A cikin daftarin sanarwar bayan taro ƙungiyar ta EU ta ce zata taka muhimmiyar rawa a wannan batu. To sai dai ba a ambaci kalmar ´yanci kai a cikin daftarin sanarwar bayan taron ba. Kasashen Cyprus da Slovanyia da Girika na ƙin duk wata shailar ´yancin kai da Kosovo zata yi daga tarayyar Sabiya. SGJ Angela Merkel ta yi kira da a samu matsayin daya dangane da wannan batu.