1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Siriya za ta yi watsi da tallafi daga Turkiya

Yusuf BalaSeptember 13, 2016

Wasu rahotanni na kafafan yada labarai na cewa akwai jirgin kayan agaji da ya nufi birnin na Aleppo daga Turkiya.

https://p.dw.com/p/1K1Vc
Libysche Flotte für Gaza
Dubban al'umma ne a yankin na Aleppo ke tsananin bukata ta tallafiHoto: AP

Gwamnatin kasar Siriya ta ce za ta yi watsi da duk wani kayan tallafi zuwa yankin Aleppo ba tare da an sanar da ita ba, ko ya bi ta hanyar Majalisar Dinkin Duniya, musamman kayan agaji da ya fito daga kasar Turkiya kamar yadda rahotanni na kafafan yada labarai suka nunar.

Ma'aikatar harkokin wajen Siriya ta ba da wannan bayani a cewar kamfanin dillancin labarai na SANA. Wannan jawabi dai na zuwa ne bayan da wasu rahotanni na kafafan yada labarai ke cewa akwai jirgin kayan agaji da ya nufi birnin na Aleppo daga Turkiya a ranar Talatan nan, abin da ke zuwa sa'oi bayan da shirin tsagaita bude wuta ya fara aiki bayan shiga tsakanin Amirka da Rasha.