1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojan Yemen sun halaka a fashewar nakiyoyi

Yusuf Bala Nayaya
April 23, 2017

Nakiyoyin ko bama-baman sun tashi ne a birnin Aden da ke kusa da gabar teku kamar yadda jami'an lafiya da masu taimakon gaggawa suka bayyana.

https://p.dw.com/p/2blBi
Jemen Milizen entfernen Landminen platziert von Houthi-Rebellen
Hoto: picture-alliance/dpa/STR

Sojojin kasar Yemen bakwai ne suka rasu baya ga wasu 15 da suka samu raunika a ranar Lahadin nan, lokacin da suke aikin kwashe wasu nakiyoyi da ake iya binnewa a kasa masu illa a lokaci da bayan yaki. Bama-baman ko nakiyoyin dai sun tashi ne a birnin Aden da ke kusa da gabar teku kamar yadda jami'an lafiya da masu taimakon gagawa suka bayyana. Wani jami'in lafiya a asibitin da aka kai marasa lafiyar da gawarwakin a yankin ya tabbatar da wannan adadi.

Birnin na Aden dai ya zama wani kwarya-kwaryar shelkwata ta mahukunta na Yemen bayan da mahukuntan bisa tallafin Saudiyya suka kakkabe 'yan tawayen daga garin da ke a gabar teku a Kudancin kasar a 2015.

Kungiyar Al-Qaeda da IS dai na amfani da damar rikicin da kasar ta Yemen ta fada ta na cin karanta babu babbaka da kara samun karfin iko a Kudanci da Gabashin na kasar ta Yemen.