1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojin mamaye za su bar Iraƙi

Ibrahim SaniNovember 27, 2007
https://p.dw.com/p/CTZS

Faraministan IraƙI Nuri- Al Maliki ya ce a shekara ta 2008 ne aikin sojin kiyaye zaman lafiya ƙarƙashin laimar Majalisar Ɗinkin Duniya ke ƙarewa a ƙasar.Bayan ficewarsu a cewar Mr Maliki, Iraƙi da mahukuntan Amirka za su ƙulla wata sabuwar yarjejeniya ta aikin kiyaye zaman lafiya a ƙasar. Rahotanni sun nunar da cewa tuni shugabannin biyu, wato Mr Bush da Al-Maliki sukayi nisa wajen tattauna wannan batu. Za a ci gaba da wannan tattaunawa ne a cewar mahukuntan na Amirka a farko-farkon sabuwar shekara, a kuma kammala a watan yuli. Dakarun sojin kiyaye zaman lafiyar na tafiyar da aikin su ne a Iraƙin ƙarƙashin jagorancin ƙasar ta Amirka ne.