1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojojin Amirka a Iraƙi sun kai samame kan ofishin wakilan Iran

January 11, 2007
https://p.dw.com/p/BuUu
Dakarun Amirka sun kai samame a ofishin karamin jakadancin Iran dake birnin Arbil na ´yan Kurdawa dake arewacin Iraqi inda suka kame mutane 5. Baya ga haka dakarun na Amirka sun kama kwace wasu takardu da na´u´rori masu kwakwalwa a yayin da hukumomin tsaro na Kurdawa suka toshe dukkan hanyoyin dake zuwa wurin da ginin yake. A martanin da ta mayar gwamnati a birnin Teheran ta kira ´yan diplomasiya dake wakiltar wasu cibiyoyin Amirka da su yi mata bayani. An kai samamen ne a daidai lokacin da Amirka ke zargin hukumomin Iran da rura wutar rikicin Iraqi tare da ba da umarnin kai hare hare akan dakarun Amirka.