1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojojin MDD hudu sun mutu a hannun Anti-Balaka

May 10, 2017

Sakatare janar na MDD ya yi Allah wadai da harin da aka kai a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, inda aka hallaka sojojij kiyaye zaman lafiya hudu wasu da dama suka jikkata

https://p.dw.com/p/2ciU1
Zentralafrikanische Republik Bangui Minusca UN-Truppen
Hoto: picture-alliance/AA/

Antonio Guterres a wata sanawar da ya fitar, yace harin an kai shi ne a kan kwambar dakarun kiyayen zaman lafiya inda nan take soja hudu suka mutu wasu kimanin 10 aka kai su babban asibiti a Bangui babban birnin Kasar. Sanarwar ta kara da cewa kawo yanzu akwai soja guda wanda ya bace bayan harin. Ana dai tuhumar 'yan kungiyar anti-Balaka da ke zama mayakan kiristoci da kai farmakin. Lamarin ya farune a kan iyakar Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya da Jamhuriyar Demokradiyyar Kwango