1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojojin Najeriya sun kashe kwamandojin Boko Haram

Abdul-raheem Hassan
August 31, 2017

Birgediya Janar Sani Usman Kuka-Sheka mai magana da amadadin rundunar, ya ce dakarun kasar sun yi nasarar kashe kusoshin kungiyar biyar tare da jikkata wasu mambobin ta Arewa maso gabashin Najeriya.

https://p.dw.com/p/2j9bZ
Nigeria Soldaten in Damboa
Hoto: Getty Images/AFP/S. Heunis

Wannan ikirarin na sojojin Najeriya na zuwane mako guda bayan da wasu 'yan kungiyar ta Boko haram kusan 70 suka mika wuya ga gwamnatin kasar, bayan wasu jerin somame da sojojin ke kaddamarwa.

Kungiyar Boko Harama dai ta zama barazana ga rayuwar fararen hula da ke yankin Arewa maso gabashin Najeriya, da ma kasahen Nijar da Chardi da ke makobtaka da kasar. To sai dai haryanzu sojojin Najeriya na kan bakansu na ganin sun murkushe ayyukan kungiyar baki daya, inda a yanzu ake saura kiris na cikar wa'adin kwanki 40 na kamo shugaban kungiyar Abubakar Shekau.