1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojojin Siriya sun kwato wani yanki daga IS

May 13, 2017

Dakarun gwamnatin Siriya sun kwato wani sansanin sojin sama na kasar daga ikon mayakan kungiyar IS, a ci gaba da fafatawar da suke yi da mayakan na tarzoma a kasar.

https://p.dw.com/p/2cv0r
Syrien Türkei YPG Kämpfer und türkische Panzer Symbolbild
Hoto: picture-alliance/AP Photo/Depo Photos/M. Corban

Gamayyar kungiyoyi da ke kare hakki jama'a a kasar Siriya ta ce mayakan da suka yi gamon taron dangi, sun danna tare da kwato sansanin na soji da ke yankin Jirrah a arewacin birnin Aleppo.

Ana dai ci gaba da gumurzu tsakanin bangarorin biyu, kamar yadda kungiyar ta tabbatar kuma ba a kai ga samun cikakkun alkaluman wadanda suka mutu a artabun na wannan Asabar.

Shaidu sun ce dakarun na ci gaba da kutsawa garin Maskanah da ake ganin babbar tunga ce ta mayakan na tarzoma a kewayen na Aleppo, inda ake ta ganin rubuce-rubucen da ke dauke da alamun kungiyar ta IS.