1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojojin Syriya na samun galaba a Aleppo

Abdul-raheem Hassan
November 28, 2016

Dakarun gwamnatin Syriya tare da hadin gwiwar sojojin kawance da ke fafatawa a gabashin birnin Aleppo sun bayyana kwace manyan yankuna masu muhimmaci da ke hannun 'yan tawayen kasar.

https://p.dw.com/p/2TNqf
Syrien Aleppo östliches Masaken Hanano Gebiet
Hoto: picture-alliance/dpa/Sana

Wata kafar yada labarun kasar Syriya ta ruwaito cewa gundumar Sakhour na cikin yankuna 10 tare da manyan gine gine 3,000 da a yanzu ke karkashin ikon dakarun gwamnatin Bashar al-Assad. Wata sanarwa da ma'akatar tsaron kasar Rasha ta fitar na cewa daruruwan 'yan tawaye na yada makamansu don ficewa daga yankin. A cewar dakarun dai wannan wata damace da zai ba su ikon nausawa yankunan da ke hannun 'yan tawayen sama da shekaru hudu.

Sai dai zafin hare-hare da ya raba birnin Aleppo gida biyu ya tilasta wa fararen hula sama 10,000 yin gudun hijira zuwa gabashin birnin. Masu ayyukan sa ido a Syriya dai na ganin cewa wannan sumame da dakarun ke kai wa shi ne irinsa mafi muni da 'yan tawayen suka fuskanta tun lokacin da suka mamaye birnin a shekara ta 2012.