1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojojin Yemen sun fatattaki 'yan Al-Qaida

Salissou BoukariApril 15, 2016

A kokarin da suke na kakkabe 'yan ta'addan Al-Qaida da suka mamaye wasu yankunan kasar, jami'an tsaron kasar Yemen na ci gaba da samun nasara kan mayakan.

https://p.dw.com/p/1IWhD
Indonesien Bandung Asien-Afrika Konferenz 1955
Hoto: National Archives of the Republic of Indonesia

Sojoji da 'yan sanda na kasar Yemen sun kori mayakan kungiyar Al-Qaida da ga birnin Houta da ke a matsayin babban birnin jihar Lahj a Kudancin kasar a wannan Jumma'a a cewar wata majiya ta jami'an tsaro.

Dakarun dai sun tashi ne daga birnin Aden zuwa Houta da ke a nisan km 30, inda suka kwaci wasu gine-gine na gwamnati tare da korar mayakan na kungiyar Al-Qaida da suka yi kaka-gida a wannan birni, kuma an samu kama wasu mayakan na 49 a cewar majiyar.

Kafin dai wannan mataki, sai da jiragen yaki na kasashen kawance da Saudiyya ke yi wa jagoranci suka shafe kwanaki biyu suna luguden wuta kan mayakan.