1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sudan ta amince da girke dakarun kungiyar AU da MDD a Darfur

June 17, 2007
https://p.dw.com/p/BuIZ

Sudan ta amince da a girke rundunar hadin guiwa ta sojojin kungiyar tarayyar Afirka da MDD a lardin Darfur mai fama da rikici dake yammacin kasar. Wakilan tawagar kwamitin sulhu suka tabbatar da haka bayan wata ganawa da suka yi da shugaban Sudan Omar Hassan al-Bashir a birnin Khartoum. Wakilan tawagar sun ce ba tare da ya gindaya wani sharadi ba, shugaba Bashir ya amince da girke rundunar da zata kunshi sojoji kimanin dubu 19. Tun a cikin makon da ya gabata Sudan ta nuna shirin amincewa da girke dakarun amma ba´a tantance kasar da zata jagoranci rundunar ba.