1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sudan ta Kudu: An gano gawar dan jarid

November 2, 2016

Kungiyar 'yan jarida ta kasa da kasa ta Reporters Sans Frontiere ta ce an gano gawar dan jaridar nan na kasar Sudan ta Kudu Isaac Vuni wanda wasu suka sace a watan Yulin da ya gabata a gidansa. 

https://p.dw.com/p/2S0g9
Südsudan Juba Militär 02/2015
Hoto: picture-alliance/AA/S. Bol

 

Kungiyar ta ce an gano gawar ce a ranar Litinin da ta gabata a cikin wata gona kusa da wani kauye mai suna Kerepi na kusa da kan iyaka da kasar Uganda inda mahaifansa ke da zama.

A ranar hudu ga watan Yulin da ya gabata ne dai wasu mutane masu sanye da kayan soja suka je gidan dan jaridar mai zaman kansa inda suka yi awon gaba da shi da wani kanensa mai suna Andruga. Kuma wasu shaidun ganin da ido sun shaida cewa mutanen da suka sace Isaac Vuni din na sanye da kayan dakaran Shugaba Salva Kiir.

Kungiyar ta RSF ta ce an kashe dan jaridar ne jim kadan bayan sace shi, sai dai kuma har yanzu babu duriyar kanan nasa da aka sace su tare. Ta kuma yi kira ga mahukuntan kasar da Sudan ta Kudu da su gaggauta bude bincike domin gano wanda ke da alhakin kisan dan jaridar dama gurfanar da shi a gaban kuliya domin hukunta shi.