1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sulhunta siyasar Kinsha ya wargaje

Usman Shehu UsmanSeptember 23, 2016

Bisa ga dukkan alamu batun sasanta rikicin kasar Jamhuriyar Demokradiyar Kwango ya sake shiga rudu bayan da bangren adawa da a farko ya shiga tattaunawar shi ma ya janye

https://p.dw.com/p/1K7F8
Demokratische Republik Kongo Protest Opposition in Kinshasa
Hoto: Reuters/K. Katombe

Tattaunawa sasanta rikicin kasar Kongo ya wargaje ne, bayan da bangaren adawan a yau Juma'a suka fidda sanarwar janyewa daga tattauanawar, inda suka ce farmakin da jami'an tsaro suka kai, wanda ya hallaka sama da mutane 50, ya nuna alamun gwamnati bata da shirin sulhu, kuma dole ake so sai shugaba Joseph Kabila ya zarce, Duk kuwa da karewar wa'adin mulkinsa. Su dai 'yan adawa na neman shugaba Kabila wanda ke mulkin kasar tun shekara ta 2001, da ya sauka daga mulkin, inda wa'adin mulkin sa ke karewa a ranar 20 ga watan Disamba, amma kuma babu ranar gudanar da sabon zabe.