1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Syria ta ba da umarnin gudanar da bincike akan kisan Hariri

October 30, 2005
https://p.dw.com/p/BvNN

Shugaban Syria Bashar al-Assad ya ba da umarnin gudanar da bincike akan kisan gillar da aka yiwa tsohon FM Lebanon Rafik Hariri. Kwamitin binciken dai zai yiwa fararen hula da jami´an sojin Syria tambayoyi sannan kuma zai ba da hadin kai ga jami´an MDD masu binciken wannan kisa. A cikin rahoton da ya gabatarwa kwamitin sulhu na MDD a kwanakin baya, mai daukaka kara na Jamus Detlev Mehlis wanda ke jagorantar binciken ya zargi manyan jami´an leken asirin Syria da na Lebanon da hannu a kisan na Hariri. Mehlis ya kuma zargi gwamnatin Damascus da rashin ba da hadin kai a binciken da yake yi. Hariri da wasu mutane 20 sun mutu a wani harin bam da aka kai a birnin Beirut a cikin watan fabrairu da ya gabata.