Taɓa Ka Lashe: 23.09.09
September 22, 2009Talla
A halin nan da ake ciki maganin gargajiya na ƙara samun karɓuwa a wurin jama´a musamman a nahiyarmu ta Afirka. Amma duk da haka masu maganin gargajiya a wannan nahiya suna kokawa saboda rashin samun wata kulawa ta a zo a gani daga wurin hukumomi. Shirin Taɓa Ka Lashe na wannan karo ya duba yadda harkaer maganin gargajiya da aka gada daga kakannin kakanni take tafiya ne a nahiyarmu ta Afirka musamman a Janhuriyar Niger.