1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taba Ka Lashe: 03.05.2017

Mohammad Nasiru Awal
May 5, 2017

Rawar da makarantun allo ke takawa wajen koyar da ilimin Al-Qurani musamman a Nijar.

https://p.dw.com/p/2cTwB

A kasashen Afirka inda musulmi ke da rinjaye irinsu Nijar makarantun allo na taka muhimmkiyar rawar gani a fannin koyar da yara maza da mata ilimin alkurani mai girma da sanin dokokin addinin musulunci da ma zamantakewa ta yau da kullum. To sai dai sau tari makarantun allon ba sa samun wata kulawa ta kirkiki ko ma wani tallafi daga hukumomi, a wasu lokutan ma korafi ake cewa suna gudana ne kara zube. Wadannan makarantun dai suna da dadadden tarihi.