1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Takaddamar shirin nukiliyar Iran

January 10, 2006
https://p.dw.com/p/BvCp

Iran ta koma ga aikin binciken a fannin nukiliya bayan ta sake bude tashar nukiliyarta ta Natanz, abin da ya janyo suka da kakkausar harshe daga ko-ina cikin duniya. Amirka ta yi gargadin cewa ana iya yin karar Iran a gaban kwamitin sulhu na MDD don kakaba mata takunkumi. Ita kuwa a nata bangaren Rasha cewa ta yi tana kokari ta shawo kan Iran da ta dakatar da binciken na fasahar nukiliya. Ministan harkokin wajen Jamus Frank-Walter Steinmeier ya ce Iran ta wuce gona da iri sannan sai ya kara da cewa zai tattauna da takwarorinsa na Birtaniya da Faransa akan ko za´a ci-gaba da shawarwari tsakanin kasashe 3 na tarayyar Turai da Iran. A cikin watan agustan bara aka dakatar da shawarwarin amma aka shirya komawa kan teburin tattaunawar a ranar 18 ga wannan wata na janeru. Shi kuwa a nasa bangaren sakataren harkokin wajen Birtaniya jack Straw ya ce kamata yayi a warware wannan takaddama ta hanyar diplomasiya amma ba da karfin soji ba.