1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Talafa wa marasa galhu a Najeriya

January 4, 2017

A Jihar Katsina ta Najeriya an girka wata kungiya mai taimakon al'umma marasa galihu.

https://p.dw.com/p/2VF1D
Kakuma Flüchtlingslager- Patienten der Augenklinik
Hoto: DW/R. Klein

Kungiyar wacce ake kira da sunan Arewa Less Previllage a turance  ta dauki nauyin yi wa mutane fiye da 700 aikin ido kyauta a fadin jihar ta katsina.Ita dai wannan kungiya ita ce ke biyan kudaden da ake yi wa al,umma gyaran ido kyauta a asibitin ido na tsohuwar kasuwa da ke cikin garin Katsina.Alh Garba Sanda Mani shi ne shugaban kungiyar:"Dama dai akwai hulda tsakanin kungiyar da asibitocin Jihar Katsina, kuma idan zan iya tunawa cikin azumin da ya wuce kungiyar ta biyawa wasu mutum hamsin aikin Ido irin wannan.''Wannan kungiya dai na samun karbuwa ga jama'a sakamakon aikin da take yi na taimaka wa jama'a a Jihar ta Katsina.