1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taliban ta kai hare-hare a Afghanistan

Suleiman BabayoJuly 1, 2016

Taliban ta dauki alhakin kai hare-hare kunar bakin wake a Afghanistan wadanda suka janyo mutuwar kusan mutane 40 tare da jikkata wasu da dama.

https://p.dw.com/p/1JH92
Afghanistan Selbstmordanschlag in Kabul
Hoto: Reuters/O. Sobhani

Mutane 37 gabilin 'yan sanda yayin da wasu kimanin 40 sun samu raunuka lokacin da kungiyar Taliban ta Afghanistan ta kai hare-hare kunar bakin wake biyu a ranar Alhamis din da ta gabata. An dai kai hare-haren ne kan tawogar motocin 'yan sanda a yammacin birnin Kabul fadar gwamnatin kasar.

A cikin wani sako ga kamfanin dillancin labaran AP, mai magana da yawun kungiyar ta Taliban ya ce su ne suka kai hare-hare. Tsagerun kungiyar Taliban suna kara kaimin kai hare-hare a cikin kasar ta Afghanistan inda zaman lafiya ke tangal-tangal.