1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tanzaniya: Dalibai sun rasa rayukansu

Ahmed Salisu
May 6, 2017

Rahotanni daga Tanzaniya na cewar yawan wadanda suka rasu sakamakon hadarin da wata mota kirar safa ta yi a arewacin kasar ya kai kimanin 32 yayin da wasu da suka jikkata ke cikin mawuyacin hali.

https://p.dw.com/p/2cXRr
Tansania tödliches Busunglück
Hoto: Getty Images/AFP/F. Rweyemamu

Wadanda wannan hadarin ya rutsa da su dai dalibai ne da shekarunsu ke tsakanin 12 zuwa 13 da malamansu biyu lokacin da suke wata ziyara a yankin nan na Arusha da akan je don yawon bude idanu. jami'an tsaro a Tanzaniya din suka ce hadarin ya auku ne lokacin da motar daliban ke saukowa daga wani tsauni inda ta fada cikin wani kogi. Yanzu haka dai jami'an sun ce suna gudanar da bincike don gano musababbin aukuwar wannan hadari.