1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tarihin Issa Hayatou

Suleiman BabayoNovember 18, 2015

Issa Hayatou ya zama shugaban wucin gadi na hukumar FIFA bayan dakatar da Sepp Blatter.

https://p.dw.com/p/1H8W5
CAF-Präsident Issa Hayatou in Marokko
Hoto: AFP/Getty Images/F. Senna

An haifi Issa Hayatou ranar 9 ga watan Agusta 1946 a garin Garwa na kasar Kameru inda yanzu yake da shekaru 69 a duniya. Hayatou ya rike mukamai daban-daban a hukumar wasan kasar ta Kameru da suka hada da shugaban hukumar wasanni ta kasa. Kuma tun ranar 10 ga watan Maris 1988 ya zama shugaban hukumar kula da wasan kwallon kafa ta nahiyar Afirka.

Yanzu haka Issa Hayatou ke rike da mukamun shugaban wucin gadi na hukumar kula da wasan kwallon kafa ta duniya FIFA, bayan dakatar da shugaban hukumar Sepp Blatter, bisa zargin cin hanci da rashawa.