1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kokarin shawo kan rikicin Siriya

Lateefa Mustapha Ja'afarDecember 18, 2015

Ministan kasashen ketare na Jamus Frank-Walter Steinmeier ya ce ya na fatan taron da za a gudanar a birnin New York na Amirka kan rikicin Siriya, zai sa a shawo kan matsalar a siyasance.

https://p.dw.com/p/1HPVm
Deutschland Frank-Walter Steinmeier Treffen der Außenminister G7 Gipfel in Lübeck
Hoto: Reuters/F. Bensch

Steinmeier ya bayyana hakan ne bayan da ya isa birnin na New York domin halaratar taron, inda ya ce muhimman matakan da ya kamata a dauka a wajen taron shi ne hanyoyin da za a bi wajen cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a tsakanin bangarorin da ke gaba da juna a Siriya. Taron dai zai samu halartar kasashe 17 ciki kuwa har da kasashe biyar masu kujerar din-din-din a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya.