1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron Charm-El Cheick a game da rikicin yankin gabas ta tsakiya

June 24, 2007
https://p.dw.com/p/BuI0

Gobe ne a birnin Charm El Cheik na ƙasar Masar, za a ganawar keke da keke tsakanin Praministan Isra´ila Ehud Olmert, da shugaban hukumar Palestinawa Mahamud Abbas, da zumar farfaɗo da batun zaman lahia a yankin gabas ta tsakiya.

Wannan taro zai wakana mako guda bayan russa gwamnatin hadin kasa da Praministan Isma´il Hanniey ya jagoranta.

A jajibirin taron, gwamnatin Isra´ila ta bayyana balle takunkumin da ta kargamawa hukumar Palestinawa, domin tallafawa Mahamud abbas ya fuskanci tawayen kungiyar Hamas, wada a halin yanzu ke rike da zirin Gaza.

Ismail Hanniey ya bayyana adawa ga wannan mataki na mika kudaden ga Mahamud Abbas, a cewar sa kudi ne , wanda dukkan Palestinawa ba tare da banbanci ba, ta kamata su mora.