1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron gaggawa kan rikicin Siriya

September 25, 2016

Kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya kira wani taron gaggawa a wannan Lahadi domin tattaunawa kan halin da ake ciki a kasar Siriya wadda ke fama da yakin basasa.

https://p.dw.com/p/2QZPx
Syrien Aleppo Kämpfe
Hoto: Getty Images/AFP/G. Ourfalian

Sakamakon yadda dakarun gwamnatin Siriya da ke samun goyon bayan sojojin Rasha ke yin ruwan bama -bamai a Aleppo inda kawo yanzu kungiyoyin farar hula da ke saka ido a Siriyar suka ce farar hula 45 suka mutu, kasashen Amirka da Birtaniya da Faransa suka ce ya kamata a kira taron domin matsa kaimi ga Rasha da ta amince a cimma shirin tsagaita wuta. A farkon wannan wata ne Amirka da Rashar suka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a Siriyar amma kuma ta wargaje mako guda bayan kai hari kan wani ayarin agaji na motocin Majalisar Dinkin Duniya.