1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron Gwamnonin arewacin Najeriya kan tsaron yankin

Kamaluddeen SaniDecember 19, 2015

Kungiyar gwamnonin arewacin tarayyar Najeriya ta gudanar da wani taro a jihar Kaduna dake arewa ta tsakiyar Najeriya da a 'yan kwanakin bayan aka samu taho mugama tsakanin 'yan shi'a da sojojin kasar.

https://p.dw.com/p/1HQXi
Kashim Shettima, Gouverneur von Borno State, Nigeria
Hoto: DW

A yayin taron shugaban kungiyar gwamnonin arewacin kasar 19 Alhaji Kassim Shettima kana gwamnan Jihar Borno ya yi nuni da cewar:

Za su duba alamarin da ya faru ta yadda hakan ba zai ba da kofar haifar da wani abu ba ga kowaye ko kuma kungiya wajen haddasa yamutsi a kowanne lungu da sako a yankin ba. Muna fama da matsalar Boko Haram da muke kokarin magance ta.

Tun da farko mai masaukin bakin Gwmanan jihar Kaduna Malam Nasir al- Rufa'i ya yi nuni da cewar sun hadu ne bisa yamutsin yan shi'a da sojojin Najeriya a inda za su dauki matakan da suka dace don kaucewa gaba.