1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron kasashen makwabtan Iraƙi akan al´amuran tsaro a kasar

March 10, 2007
https://p.dw.com/p/BuQ4
A wani lokaci yau wakilai daga kasashe da kungiyoyi 16 zasu tattauna a Bagadaza don neman mafita daga jerin tashe tashen hankula da rashin tsaro a Iraqi. Daga cikin mahalarta taron inda za´a tattauna kan al´amuran tsaro a Iraqi, akwai jami´an diplomasiya na makwabtan kasar da na kasashe biyar masu kujerun dindindin a kwamitin sulhun MDD. A karon farko taron zai ba da damar zama kan teburi guda tsakanin wakilan Amirka da na Iran da kuma na Syria. FM Iraqi Nuri Al-Maliki ya bayyana haka da cewa wata alama ce ta samar da zaman lafiya a kasar sa. To amma ministan harkokin waje Hoshiyar Sebari ya ce taron kadai ba zai warware matsalolin kasar ba. A wani labarin kuma dakarun gwamnatin Iraqi sun ce sun kame shugaban wata kungiyar ´yan takife ta ´yan sunni a yammacin birnin Bagadaza. Gidan telebijin Iraqi ta bayyana wannan mutumin da Abu Omar al-Baghdadi, wanda aka yi imani cewar shi ne jagoran wata kungiyar ´yan tawaye dake kiran kanta kasar Islamiya ta Iraqi.